Sojoji sun kashe ƴan bindiga 7 a Kaduna

Sojojin rundunar samar da tsaro ta Operation Safe Haven sun kashe yan bindiga 7 tare da gano makamai a ƙaramar hukumar Zangon Kataf ta jihar Kaduna.

A wata sanarwa ranar Talata mai magana da yawun rundunar, Kyaftin Oya James ya ce sojojin dake gudanar da sintiri sun yi arba da yan bindigar ne a wurin da ake kira tudun Kachalla inda aka yi musayar wutar da ta kai ga kisan ƴan bindiga shida a yayin da wasu suka tsere da raunin harbin bindiga.

Sanarwar ta ce an gano bindigar AK-47, harsashi masu yawa, waya kirar Tecno, babur da sauran abubuwa biyo bayan binciken wurin da aka yi artabun da sojoji suka yi.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma kashe wani sanannen dan bindiga da ake kira da Musa Wada a ƙauyen Kondo dake ƙaramar hukumar.

Sanarwar ta cigaba da cewa mutane 33 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban aka kama a cikin makon da ya wuce.

More News

Matatar mai ta fatakwal za ta iya fara aiki a ƙarshen watan Yuni

Matatar mai ta Fatakwal mai tace mai ganga 210,000 a kowacce rana na iya fara aiki a karshen watan Yuli bayan dogon lokaci. Jami’in hulda...

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa  a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...