Ƴan Bindiga Sun Kashe Akalla 32 A Harin Kebbe



Aƙalla mutum 32 ne ake zargin ’yan bindiga sun kashe a wani hari da suka kai garin Ungushi da wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar Kebbe ta jihar Sokoto.

Mazauna yankin sun ce maharan sun shafe sa’o’i suna kai hare-hare, inda wasu mazauna garin suka yi musayar wuta da su tare da kashe ’yan bindiga 13.

Wani mazauni ya ce maharan sun shiga Ungushi da misalin ƙarfe 2:15 na ranar Juma’a, lokacin da ake gudanar da sallar Juma’a. Ya ce sun ajiye babura a gaban masallaci, suka tarwatsa masu ibada, sannan suka shiga cikin garin inda suka kashe mutum biyar.

A cewarsa, maharan sun sake dawowa bayan sun tafi, inda suka kashe wasu mutane biyu. Daga nan suka kewaye garin tare da ci gaba da harbe-harbe, lamarin da ya sa wasu mazauna suka gudu zuwa gidaje ko tsauni domin tsira.

Ya ce ’yan bindigar sun ci gaba da kasancewa a yankin har zuwa kusan ƙarfe 1 na dare, sannan suka sake dawowa da safe inda suka ci gaba da kashe mutane, kafin jami’an tsaro su isa wurin.

Harin ya kuma shafi ƙauyukan Umbutu, Maikurhuna, Gwandi, Girkau da Zugu, inda aka sace dabbobi da wasu kayayyaki.

Sai dai rundunar ’yan sandan jihar Sokoto ta ce ba ta da cikakken bayani kan adadin mutanen da aka kashe.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...