
Yan bindiga sun yi garkuwa da Faruk Hassan Bunza alkalin babban kotun jihar Kebbi.
An yi awon gaba da alkalin ne da tsakar daren ranar Lahadi daga gidansa dake kan titin Zogirma a karamar hukumar Bunza ta jihar Kebbi.
Wasu majiyoyi sun shedawa jaridar Daily Trust cewa an kai farmaki gidan ne da misalin ƙarfe 12:00 na daren ranar Asabar jim kaɗan bayan da alkalin ya dawo daga jihar Sokoto
“Ya dawo kenan daga jihar Sokoto lokacin da yan bindigar suka farma gidan su ka yi awon gaba da shi,” a cewar majiyar.
Ya kara da cewa babu wanda ya jikkata a cikin iyalan gidan a lokacin da yan bindigar su ke harbin kan me uwa da wabi.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kebbi, SP Bashir Usman ya tabbatar da faruwar lamarin lokacin da yake zantawa da wakilin jaridar Daily Trust.

