Wani matashi  ya kashe mahaifiyarsa mai shekaru 60 da adda

Sulaiman SaadHausa47 minutes ago

Rundunar ƴan sandan jihar Ondo ta kama wani matashi mai shekaru 23 mai suna, Samuel Akoade bayan da ra zarge shi da kashe mahaifiyarsa mai suna, Mrs Olufunke Ore dake Ore a karamar hukumar Odigbo ta jihar.

Rundunar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta kamar yadda jaridar Daily Trust ta ce lamarin ya faru ranar Lahadi 16 ga watan Agusta.

A cewar yan sandan an gano gawar matar mai shekaru 60 a cikin gidanta kwance cikin jini male-male ɗauke da sara na adda.

Jami’an ƴan sanda daga ofishin ƴan sanda dake Ore sun isa tare da killace wurin bayan samun labarin inda suka kuma ƙaddamar da bincike.

Sanarwar ta ce an samu wata adda da ake zargin an yi amfani da ita wajen kisan a wurin  yayi da wanda ake zargi ya cika wandonsa da iska.

Biyo bayan bin diddigi tare da bincike  ƴan sandan sun samu nasarar kama Samuel Akoade.

“Tuni aka ajiye gawar marigayiyar  a dakin ajiye gawarwaki a yayin da ake tsare da wanda ake zargin.An kuma mika batun ga sashen binciken manyan laifuka na rundunar yan sandan jihar,” a cewar sanarwar.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...