Mutane 300 Sun Yi Zanga-Zangar A Kori Baƙin Da Ba Su Da Takardun Zama A Afirka Ta Kudu

Muhammadu SabiuHausa17 minutes ago



Akalla mutane 300 ne suka gudanar da zanga-zanga a wajen taron shugabannin ƙasashen Kudancin Afirka (SADC) a Durban, Afirka ta Kudu, domin neman a kori baƙin da ba su da takardun zama a ƙasar.

Jagorar masu zanga-zangar, Jacinta Ngobese-Zuma, ta ce sun je wurin ne domin isar da saƙo ga shugabannin SADC kan bukatar ƙasashen yankin su dawo da ‘yan ƙasarsu da ke zaune a Afirka ta Kudu ba bisa ƙa’ida ba.

Zanga-zangar ta zo ne bayan dubban ‘yan ƙasashen waje sun fice daga Afirka ta Kudu a cikin watannin baya saboda rikicin ƙyamar baƙi, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...