Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya yi Allah wadai da hare-hare da cin zarafin baƙi da ake yi a wasu yankunan ƙasar.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ramaphosa ya ce gwamnatin ƙasar ba ta da hannu a irin waɗannan ayyuka, tare da kira ga jama’a su kasance masu bin doka da oda.
Ya jaddada cewa gwamnati ba za ta lamunci miyagun laifukan da ake aikatawa kan baƙi ba.
A kwanakin baya, ƙasashen Ghana da Najeriya sun nuna damuwa kan yadda aka rika cin zarafin ’yan ƙasashensu da ke zaune a Afirka ta Kudu.
Hukumomin Ghana da Najeriya sun kuma bayyana cewa suna taimaka wa wasu daga cikin ’yan ƙasarsu da ke son komawa gida.
Shugaban Afirka ta Kudu Ramaphosa Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Baƙi a Ƙasarsa

