Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi, ya bayyana cewa babu wani laifi idan malamai suka shiga siyasa domin ba da gudummawa wajen inganta shugabanci.
Gumi ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, yayin da ake ci gaba da muhawara kan ko ya dace malamai su tsaya ga wa’azi ko kuma su shiga siyasa.
Muhawarar ta ƙara ɗaukar hankali bayan tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami, ya zama ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe na jam’iyyar PDP.
A cewar Gumi, “Malamin addini da ya shiga siyasa ya ɗauki wahalhalunta ya fi wanda yake zaune a kan darduma yana yi wa ‘yan siyasa addu’a.”
Gumi Ya Goyi Bayan Shigar Malamai Siyasa

