Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya isa birnin Najaf na ƙasar Iraƙi domin halartar bikin Arbaeen, kamar yadda hukumomin Iran suka tabbatar.
Araqchi ya wallafa hotonsa bayan saukarsa a Najaf ta shafinsa na Telegram.
Ziyarar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce za a fara tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a ranar Litinin. Sai dai kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce ba su da wani bayani kan sanarwar da Trump ya yi game da tattaunawar.
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Isa Iraƙi Domin Bikin Arbaeen

