ICPC Ta Kammala Bincike Kan Hukumar Gwamnatin Tarayya Ta Bogi




Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta kammala bincikenta kan cece-ku-cen da ya shafi cibiyar Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC), wadda ake zargin ba ta da sahihanci.

Rahotanni sun ce an yi wa babban wanda ake zargi, Prince Adeniyi Adeyemi, tambayoyi bayan kama shi, kuma ana kan kammala rahoton da za a miƙa wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu cikin wa’adin da ya bayar.

A nasa ɓangaren, Kwamitin Musamman na Majalisar Wakilai da ke binciken lamarin ya bayyana cewa zai sanar da jama’a sakamakon bincikensa a wannan makon kafin ya gabatar da cikakken rahoto ga majalisar.

Sai dai Adeyemi ya musanta cewa shi kaɗai ne ya ƙirƙiri cibiyar, yana mai cewa hukumomin gwamnati da dama sun yi mu’amala da ita. Ya kuma buƙaci a ba shi damar bayyana matsayinsa kafin a kammala binciken.

Haka kuma, Cibiyar Centre for Democracy and Development (CDD) ta buƙaci kwamitin majalisar ya bai wa Adeyemi damar kare kansa domin tabbatar da adalci da sahihancin rahoton binciken.

More from this stream

Recomended