Iyalan Alƙalin Kebbi Sun Tabbatar Da Biyan Naira Miliyan 50 Domin Sakinsa



Iyalan Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruk Hassan Bunza, sun tabbatar da cewa sun biya Naira miliyan 50 ga masu garkuwa da mutane domin samun sakinsa.

An sace Mai Shari’ar ne daga gidansa da ke ƙaramar hukumar Bunza a ranar 26 ga Yuli, inda ya shafe kwanaki takwas a hannun ‘yan bindiga kafin a sake shi a ranar Litinin.

Wani ɗan uwansa ya bayyana cewa masu garkuwar sun fara neman Naira miliyan 200, amma daga baya suka amince da karɓar miliyan 50 bayan tattaunawa.

Sai dai Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi ta tabbatar da sakin alƙalin, tare da jaddada cewa tana adawa da biyan kuɗin fansa. Rundunar ta ce tana ci gaba da bincike domin cafke waɗanda suka aikata laifin.

Kungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta kuma yi Allah wadai da sace alƙalin, inda ta buƙaci a ƙara tsaurara matakan tsaron jami’an shari’a a faɗin ƙasar.

More from this stream

Recomended