Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Sarkin Ode Oriya da ke Karamar Hukumar Owo a Jihar Ondo, Adeniyi Adelana.
Rahotanni sun ce maharan kusan shida dauke da makamai sun kai hari gidan sarkin da misalin karfe takwas da rabi na dare a ranar Asabar. Sun harbi matarsa kafin su tafi da shi zuwa cikin daji.
Jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ondo, Abayomi Jimoh, ya tabbatar da aukuwar lamarin. Ya ce matar sarkin na samun kulawa a wani asibiti.
Ya kuma bayyana cewa jami’an tsaro sun fara aikin bincike da ceto, inda suke sintirin dazuka da hanyoyin da ake zargin maharan sun bi domin ceto sarkin tare da cafke wadanda suka aikata laifin.
Rundunar ‘yan sandan ta bukaci mazauna yankin su ci gaba da gudanar da harkokinsu cikin kwanciyar hankali tare da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanan da za su taimaka wajen gudanar da binciken.
Ƴan Bindiga Sun Sace Wani Basarake Tare Da Harbin Matarsa

