
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Najeriya (INEC) ta bayyana cewa a yau Laraba, 19 ga Agusta 2026, za a fara yakin neman zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a hukumance.
Mai magana da yawun INEC, Zainab Aminu Abubakar, ta ce dokar Zabe ta 2026 ta tanadi cewa jam’iyyun siyasa su fara yakin neman zaben wadannan kujeru kwanaki 150 kafin ranar kada kuri’a.
Ta ce za a gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan Majalisar Dattawa da ta Wakilai a ranar 14 ga Janairu 2027.
A gefe guda, INEC ta tsara fara yakin neman zaben gwamnonin jihohi da ‘yan majalisun jihohi a ranar 9 ga Satumba 2026, yayin da za a gudanar da zabukan a ranar 6 ga Fabrairu 2027.