ASUU: Malamai Kimanin 200 Sun Bar Jami’ar Kaduna

Muhammadu SabiuHausa18 minutes ago



Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), ta bayyana cewa kimanin malamai 200 ne suka bar aiki a jami’ar saboda rashin kyakkyawar walwala.

Shugaban ASUU na KASU, Dr Abubakar Abdullahi, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai, inda ya ce daga cikin malaman da suka bar jami’ar har da farfesoshi da sauran manyan malamai.

Ya ce yawan barin aikin na iya yin illa ga ingancin koyarwa da bincike, tare da kawo cikas ga ci gaban jami’ar.

Ƙungiyar ta danganta lamarin da rashin ingantaccen yanayin walwala da kuma gazawar gwamnatin Jihar Kaduna wajen aiwatar da wasu yarjejeniyoyin da suka shafi jin daɗin ma’aikata.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...