

Nyesom Wike ministan babban birnin tarayya Abuja ya bayar da umarni da ayi gaggawar rushe gidajen da suka tare magudanar ruwa dake unguwar Maitama da kuma sauran wuraren dake fuskantar ambaliyar ruwa a birnin tarayya Abuja.
Wike ya bayar da umarnin ne a ranar Talata bayan da ya ziyarci wuraren da ambaliyar ruwan ta shafa a unguwar Maitama.
Ya ce za a fara rushe-rushen ba tare da bata lokaci ba za kuma a cigaba har ya zuwa ranar Asabar ba tare da la’akari da siyasa ko kuma matsayin mutanen da su ka mallaki gine-ginen da abin ya shafa.
Umarnin ministan na zuwa ne bayan da ambaliyar ruwa ta shafi wani ɓangare na birnin biyo bayan mamakon ruwan sama da aka maka.
Masana da dama sun alakanta ambaliyar ruwa da gine-gine da aka yi kan hanyoyi da kuma yadda aka mayar da wasu filaye ya zuwa gidaje ba kamar yadda ainihin taswirar birnin ta tanada ba.