

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar Talata ya yi wata ganawar sirri da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio a fadar shugaban ƙasa ta Aso Rock dake Abuja
A cewar rahotanni, Akpabio ya isa fadar Aso Rock da misalin karfe 06:12 na yamma inda ya ya haɗu da shugaban ƙasar da a dai-dai lokacin ya ke tsaka da ganawa da Mohammed Idris ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a.
Kusan sa’a guda bayan zuwan Akpabio sai aka hangi ministan tattalin arzikin cikin tekun, Gboyega Oyetola ya iso fadar shugaban ƙasar tare da Hon Alhassan Ado Doguwa ɗan majalisar wakilai ta tarayya dake wakiltar ƙananan hukumomin Tudunwada da Doguwa.
Har ila duk a lokacin an hangi ministan ma’dadinai, Dele Alake a fadar shugaban kasar.
Duk da cewa babu wani dalili da aka bayyana na ziyarar ta su a fadar shugaban ƙasar, ziyarar Oyetola na zuwa ne yan kwanakin kaɗan bayan sake zaɓen Ademola Adeleke mutumin da ya gaji kujerar gwamnan jihar Osun bayan da ya kayar da shi a zaɓen 2022.