An Harbe Sanannen Malamin Addini A Pakistan



Ƴan sanda a ƙasar Pakistan sun tabbatar da cewa wasu ƴan bindiga sun kashe wani fitaccen malamin addinin Musulunci a lardin Khyber Pakhtunkhwa da ke arewa maso yammacin ƙasar.

Rahotanni sun ce Maulana Muhammad Idrees na kan hanyarsa ta komawa gida ne daga wata makarantar koyar da addini, lokacin da ƴan bindigar da ke kan babura biyu suka buɗe masa wuta, inda suka kashe shi nan take.

Harin ya faru ne a yankin Charsadda, inda kuma aka jikkata ƴan sanda biyu da ke cikin tawagar da ke ba shi tsaro.

Ya zuwa yanzu babu wata ƙungiya da ta fito ta ɗauki alhakin kai harin. Sai dai galibi ana danganta irin waɗannan hare-hare da masu tsatsauran ra’ayin addinin Musulunci.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]