Ƴan Sanda Sun Kama Mutane 2 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Zargin Garkuwa Da Mutane



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Anambra ta sanar da kama wasu mutane 2 da ake nema ruwa a jallo bisa zargin hannu a ayyukan garkuwa da mutane a jihar.

Kakakin rundunar, SP Tochukwu Ikenga, ya ce jami’an Rundunar Gaggawa ta Awkuzu ne suka gudanar da samamen bayan samun sahihan bayanan sirri, inda suka kama Dauda Mohamed.

A cewarsa, wanda ake zargin ya amsa cewa yana cikin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ke Jihar Kogi, tare da bayyana sunayen wasu mambobin ƙungiyar da har yanzu ba a kama ba.

Binciken ‘yan sanda ya kuma nuna cewa ana zargin Dauda Mohamed da hannu a sace wani mutum daga Divine Heritage Lodge da ke garin Ukwulu, inda masu garkuwa da mutanen suka buƙaci a biya kuɗin fansa har Naira miliyan 30 kafin su sake shi.

More from this stream

Recomended