Atiku Ya Ce Bai Yi Nadamar Hana Yunƙurin Wa’adi Na Uku Na Obasanjo Ba


Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa bai da wani nadama kan adawa da yunƙurin tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, na neman wa’adi na uku a mulki.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar domin mayar da martani ga kalaman Obasanjo, wanda ya ce ya yi nadamar zaɓar Atiku a matsayin mataimakinsa lokacin da suke mulki tsakanin 1999 da 2007.

Atiku ya ce yana alfahari da tsayawa kan kare kundin tsarin mulkin Najeriya da kuma hana duk wani yunƙuri na tauye dimokuraɗiyya saboda muradin siyasa.

Ya kuma ce ya taka muhimmiyar rawa wajen taimaka wa Obasanjo lokacin da yake fuskantar matsaloli kafin ya zama shugaban ƙasa, yana mai ƙara da cewa bai yi nadamar wannan taimako ba.

Atiku ya bukaci shugabannin ƙasar su mayar da hankali kan magance matsalolin tattalin arziki, rashin tsaro da rashin aikin yi, maimakon ci gaba da tayar da tsoffin saɓanin siyasa.

More from this stream

Recomended