‘Yan Sandan Yobe Sun Kama Mutane 448, An Kuma Yanke Wa 152 Hukunci Cikin Shekara Guda



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Yobe ta bayyana cewa ta gudanar da bincike kan shari’o’i 407 tare da kama mutane 448 da ake zargi da aikata laifuffuka daban-daban cikin shekara guda.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Usman Kanfani Jibrin, ya bayyana hakan a hedikwatar rundunar da ke Damaturu. Ya ce daga cikin shari’o’in akwai kisan kai 31, fyade 35, satar mutane 8, fashi da makami 11 da kuma wasu laifuffuka 322.

Ya ƙara da cewa kotu ta yanke wa mutane 152 hukunci, yayin da wasu shari’o’i ke ci gaba da gudana a kotuna.

Rundunar ta kuma ce ta gano wani wurin ajiyar miyagun ƙwayoyi a Potiskum, inda ta kama wanda ake zargi da jagorantar harkar tare da ƙwato nau’o’in miyagun ƙwayoyi da kuɗi N835,500 da ake zargin an samu daga safarar ƙwayoyi.

Haka kuma, jami’an ‘yan sanda sun kai samame a maɓoyar masu laifi a ƙaramar hukumar Jakusko, inda suka kama mutane 14 da ake zargi da safara da amfani da miyagun ƙwayoyi, tare da ƙwato haramtattun ƙwayoyi masu yawa.

Kwamishinan ya jaddada aniyar rundunar na ci gaba da yaƙi da aikata laifuffuka da kuma kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...