Masu garkuwa da mutane sun sako mai shari’a Bunza

Masu garkuwa da mutane sun sako, Faruk Bunza alkalin babbar kotun jihar Kebbi da su ka yi garkuwa da shi.

A ranar 26 ga watan Yuli ne aka yi garkuwa da mai shari’a Bunza a gidansa dake kan titin Zogirma a karamar hukumar Bunza ta jihar.

An yi garkuwa da shi ne jim kaɗan bayan ya dawo daga jihar Sokoto.

Ranar 3 ga watan Agusta ne aka sako shi.

Da yake tabbatar da sakin nasa a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kebbi,Bashir Usman ya ce iyalansa da kuma hukumar shari’a ta jihar Kebbi sun tabbatar da sakin nasa.

Sai dai mai magana da yawun ya ki bayyana ko an biya kuɗin fansa ko ba a biya ba kafin sakin nasa.

Sanarwar ta kara da cewa rundunar yan sandan za ta cigaba da ƙoƙarin bin diddigin waɗanda su ka yi garkuwar domin kama su da gurfanar da su gaban shari’a.

More from this stream

Recomended