Yan sanda sun kai farmaki maboyar masu garkuwa da mutane a Enugu

Rundunar ƴan sandan jihar Enugu ta ce jami’anta sun kai samame wata maboyar masu garkuwa da mutane dake cikin wani daji akan hanyar Amufie-Obollo Affor a karamar hukumar Igbo Eze ta jihar inda suka gano harsashi, babur na hawa bayan da su ka yi musayar wuta da mutanen.

A wata sanarwa ranar Laraba, Daniel Ndukwe mai magana da yawun rundunar ya ce an kai samamen ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 07:40 na dare biyo bayan umarnin da kwamishinan yan sandan jihar, Mamman Giwa ya bayar.

” A yayin samamen jami’an yan sanda sun yi arangama da wasu batagari ɗauke da makamai da ake zargin masu garkuwa da mutane ne wanda suka buɗe wuta bayan da suka hangi jami’an tsaro,” a cewar sanarwar.

Ndukwe ya  ya kara da cewa jami’an tsaron sun mayar da martani abun da ya tilastawa yan bindigar tserewa.

Binciken da aka gudanar a maboyar ya kai ga  gano bindiga ƙirar AK-47 guda biyu, gidan zuba harsashi guda huɗu, harsashi guda 64 da kuma babur ƙirar TVS Neo guda ɗaya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]