
Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta ce jami’anta sun kama wata babbar mota mai dauke da kakin sojoji da kuma katan katan na haramtattun kwayoyin da ake shirin kai su yankin kudu maso gabas.
Da yake magana a yayin wani taron manema labarai a ranar Talata, Tijani Fatai kwamishinan yan sanda na jihar Lagos ya ce an kama motar ne a yankin Lekki-Epe akan hanyarta ta ficewa daga birnin.
Fatai ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike domin gano daga inda kayan suka fito da kuma wanda za a kai wa su.
Kwamishinan ya kara da cewa an kama mutane uku da ake zargi da ɗauko kayan.
” binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wa motar da aka gano ana zargin yin amfani da ita wajen safarar kakakin soja zuwa yankin kudu maso gabashin Najeriya,” ya ce.

