Radda ya yi kira da a yiwa jihar Katsina addu’a

Gwamnan jihar Katsina,Dikko Umar Radda ya shawarci mazauna jihar da kada su siyasantar da matsalar tsaron jihar maimakon haka su ƙara yawan addu’a domin samun zaman lafiya mai ɗorewa tare da taimakawa jami’an tsaro a ƙoƙarin da su ke na samar da zaman lafiya.

Gwamnan ya yi wannan rokon ne a Katsina a wurin taron ranar Yaumul Shakur ta shekarar 2026 da aka gudanar domin tunawa da  ranar da aka haɗe Lardin Katsina da Daura a shekarar 1934.

Radda ya ce matsalar tsaro kalubale ne da ya shafi al’umma baki ɗaya dake buƙatar haɗin kai da addu’a maimakon siyasantar da batun.

“Wannan tattaruwa da muka yi ba taro bane kadai al’ada ce ta nuna godiya da kakannin mu suka kafa. Shi ya sa muka saka ranar 1 ga watan Agusta na kowace shekara a matsayin Yaumul Shukur domin godewa Allah da kuma neman kariyarsa ga jihar mu,” a cewar Radda.

Ya bayyana Katsina a matsayin jiha da Allah Ya  albarkace da ƴaƴa nagari maza da mata da su ka bada gagarumar gudummawa wajen cigaban Najeriya.

He described Katsina as a state blessed with accomplished sons and daughters who have made significant contributions to Nigeria and beyond

More from this stream

Recomended