Akalla gidaje sama da 200 ne suka rushe sakamakon ruwan sama mai tafe da iska mai ƙarfi da ya afku a ƙaramar hukumar Kusada da ke jihar Katsina.
Lamarin ya kuma lalata shaguna da dama, inda ya jawo asarar dukiya mai yawa. Sai dai babu rahoton rasa rayuka zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Mafi yawan barnar ta auku ne a garuruwan Janbango, Dangamau da Kusada, inda iyalai da dama suka rasa matsugunansu tare da fuskantar ƙarancin abinci da sutura.
Tun da farko, Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi gargaɗin yiwuwar samun ambaliyar ruwa a jihohi daban-daban na ƙasar a cikin watan Yuli.
Ruwan Sama Da Iska Sun Rusa Gidaje Sama Da 200 A Katsina

