Aƙalla mutane 97 sun mutu sakamakon ambaliyar ruwa a Jihar Assam da ke arewa maso gabashin Indiya, yayin da kusan mutane 170,000 suka fuskanci matsalar ambaliyar.
Ambaliyar ta mamaye gidaje da gonaki, tare da tilasta dubban mutane barin muhallansu zuwa sansanonin wucin gadi.
Rahotanni sun ce ruwan ya mamaye fiye da kadada 14,000 na gonaki, yayin da wasu yankuna suka nutse cikin ruwa da taɓo.
Firaministan Assam, Himanta Biswa Sarma, ya jajanta wa iyalan wani yaro mai shekara 13 da ya rasu yayin ƙoƙarin ceto karensa daga ruwan ambaliyar.
Ministan Lafiya na Indiya, J.P. Nadda, wanda ya ziyarci yankin, ya ce girman barnar ya yi yawa, kuma zai ɗauki lokaci kafin al’amura su koma daidai.
“Kauye guda bayan ƙauye duk sun nutse a ruwa,” in ji shi.
Ambaliyar ruwa ta zama ruwan dare a Assam a lokacin damina, musamman daga Yuni zuwa Satumba, yayin da Kogin Brahmaputra da sauran rassansa ke cika.
Masana sun ce sauyin yanayi da rashin kyakkyawan tsarin ayyukan ci gaba na ƙara tsananta irin waɗannan ambaliyar ruwa.
Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Kusan Mutum 100 A Indiya

