Jami’an tsaro sun kashe yan bindiga 24 a Katsina

Akalla yan fashin daji 24 ne aka kashe bayan da jami’an tsaro suka dakile wani yunkurin yin garkuwa da mazauna kauyen Gidan Bawa dake mazabar Ƙandarawa a karamar hukumar Bakori ta jihar Katsina.

A cewar kafar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin Tafkin Chadi aƙalla ƴan bindiga kusan 40 dake biyayya ga gawurtaccen dan fashin daji, Isiya Kwashen Garwa ne suka mamaye kauyen a  ranar Talata inda suka yi kokarin yin garkuwa da mutane musamman mata da ƙananan yara.

Kafar labaran ta bayyana cewa farmakin da  jami’an tsaron suka kai wa maharan ya haɗa da jami’an DSS, sojoji da kuma dakarun sakai na hukumar Katsina Community Watch Corps.

Zagazola Makama ya kara da cewa yan bindigar sun shirya yin garkuwa da mutane masu yawa ne kamar yadda su ka yi a g garin Woro dake jihar Kwara.

A cewar Makama bayanan sirrin da jami’an tsaro suka samu  sun nuna cewa yan ta’addar sun shirya yin garkuwar ne domin su muzata da kuma kunyata gwamnati.

Bayanan sirrin da jami’an  DSS suka samu ne ya saka suka tattara kan jami’an soja da na Civilian JTF inda suka yi musu kwanton bauna har ta kai ga sun kashe 24 daga cikin ƴan bindigar.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...