Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci wata tawaga zuwa hedkwatar kamfanin Huawei da ke birnin Shenzhen na ƙasar Sin domin tattauna yiwuwar haɗin gwiwa wajen bunƙasa fasahar zamani a jihar.
A yayin ganawar, gwamnatin Zamfara ta gabatar da shirinta na amfani da fasahar zamani wajen inganta gudanar da mulki, ƙarfafa tsaro da kuma faɗaɗa hanyoyin sadarwa.
A cewar wata sanarwa da babban sakataren Hukumar Bunƙasa Fasahar Zamani ta Jihar Zamfara, Habib Gajam, ya wallafa a shafinsa na Facebook, jami’an Huawei sun bayyana fasahohin da kamfanin ke da su da kuma nasarorin da ya samu wajen aiwatar da ayyukan gwamnati na zamani a ƙasashe daban-daban.
Gwamnatin jihar ta ce tana fatan tattaunawar za ta haifar da ayyukan da za su bunƙasa tattalin arziki, inganta rayuwar al’umma, tare da mayar da Zamfara ɗaya daga cikin cibiyoyin fasaha da ƙirƙire-ƙirƙire a Arewacin Najeriya.
Gwamnan Zamfara Ya Tattauna Da Huawei Kan Bunƙasa Fasahar Zamani

