Ofisoshin jakadancin Amurka da ke Bagadaza da Erbil sun gargaɗi ’yan ƙasar Amurka da ke Gabas ta Tsakiya da su kasance cikin shirin ficewa daga yankin idan rikicin tsaro ya ƙara tsananta.
A cikin sanarwar tsaro da suka fitar, ofisoshin jakadancin sun ce rikicin da ke ƙara ƙamari a yankin ya sa yanayin tsaro ya zama mai sarƙakiya, tare da yiwuwar ƙara taɓarɓarewar lamura.
Sanarwar ta kuma yi gargaɗin cewa ana iya soke zirga-zirgar jiragen sama, a rufe sararin samaniya na wucin gadi, tare da samun tangarda a tafiye-tafiye.
Haka kuma, ta buƙaci ’yan Amurka da ke yankin su yi la’akari da ficewa ko kuma su kasance cikin shirin barin yankin idan rikicin ya ƙara tsananta.
Ofisoshin jakadancin Amurka da ke Amman a Jordan da kuma Urushalima ma sun fitar da irin wannan gargaɗin.
Amurka Ta Gargaɗi ’Yan Ƙasarta Da Su Shirya Ficewa Daga Gabas Ta Tsakiya

