Rundunar sojin Najeriya ta ce matar wani babban jami’in kula da harkokin kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP tare da ɗanta mai shekara 11 sun miƙa wuya ga dakarun Operation Hadin Kai a ƙauyen Kusuma da ke Jihar Borno.
A cewar rundunar, binciken farko ya nuna cewa mijin matar, wanda ya kasance babban kwamandan ISWAP, ya miƙa wuya tun ranar 25 ga Yuli. Sojojin sun ce shi ne ya umarce ta da ta fito daga maɓoyarsu tare da ɗansu domin su miƙa wuya.
Haka kuma, rundunar ta ce a wani samame da ta kai a yankin Turoh bayan samun sahihan bayanan sirri, mayaƙan ISWAP sun tsere kafin isowar dakarun.
Bayan binciken yankin, sojojin sun ce sun kwato babura biyu da kuma tarin miyagun ƙwayoyi da mayaƙan suka bari a baya. Rundunar ta ƙara da cewa za ta ci gaba da ƙarfafa hare-haren da suka dogara da sahihan bayanan sirri domin yaƙi da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.
Matar Babban Jami’in ISWAP Da Ɗanta Sun Miƙa Wuya Ga Sojoji A Borno

