Rahotanni sun bayyana cewa mayakan kungiyar ISWAP sun kai harin kwanton bauna kan bangaren Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS) a yankin Bula Murge da ke karamar hukumar Bama ta jihar Borno.
A cewar masanin harkokin tsaro Zagazola Makama, harin ya yi sanadin mutuwar wasu manyan kwamandojin JAS, ciki har da Abu Ubaida, Modu Kori, Alhaji Modu, Mure, Zarkawi, Sheriff da Modu Maye.
Rahoton ya kuma ce mayakan JAS da suka tsira sun fara kwashe iyalansu zuwa Bula Daloye bayan da aka lalata sansanoninsu tare da kona muhimman wuraren da suke amfani da su.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa wannan rikicin ya kara raunana JAS, kuma ya ba sojoji damar kara kaimi wajen yaki da kungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin. Haka kuma, an umarci dakarun da ke aiki a Bama da wasu yankunan makwabta su ci gaba da kai hare-hare domin hana kowace kungiyar sake karfafa kanta.
lSWAP Ta HaIIaka Manyan Kwamandojin JAS A Hqrin Kwanton Bauna A Borno

