
Rundunar sojan saman Najeriya ta ce dakarun ta dake aiki karkashin rundunar Operation Hadin Kai sun kai wani farmaki ta sama da ya kashe mayakan kungiyar ISWAP da dama a yankin Tafkin Chadi.
Wasu majiyoyin na jami’an leken asiri na soja sun fadawa kafar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin Tafkin Chadi cewa farmakin ya halaka wani babban kwamanda a kungiyar ta ISWAP tare da kashe wasu mayaÆ™a huÉ—u ciki har da wanda ya dade yana karabarwa kungiyar harajin kamun kifi.
Bayanan harin da aka tattara sun nuna cewa, Ba Ari Hisbah wanda shi ne shugaban sashen yan sanda na ISWAP a yankin Tafkin Chadi ya samu munanan raunuka a ƙafafunsa biyu bayan harin da aka kai kusa da Arege a ranar 5 ga watan Agusta.
Farmakin ta sama wani É“angare ne na cigaba da zafafa kai hare-hare kan yan ta’adda dake yankin na Tafkin Chadi.

