Sojoji Sun Sanya Tukuici Ga Duk Wanda Ya Fallasa Manyan Shugabannin ISWAP Da Ake Nema



Rundunar Operation Hadin Kai ta ayyana wasu manyan shugabannin kungiyar ISWAP a matsayin wadanda ake nema bayan ta gano bayanansu daga na’urorin sadarwa da aka kwato a wani samame da aka kai a yankin Tafkin Chadi da ke Jihar Borno.

A cewar rundunar, binciken da aka gudanar kan na’urorin ya taimaka wajen gano wuraren da ‘yan ta’addan ke amfani da su da kuma wasu manyan jagororinsu. Daga cikin wadanda aka bayyana akwai shugaban kungiyar, Abu Musa Al-Mangawi Baa Shuwa, da mataimakinsa Muhammad Jidda, tare da wasu kwamandoji.

Rundunar ta ce za ta bayar da lada mai tsoka ga duk wanda bayanansa suka kai ga kama Abu Musa. Haka kuma, an sanya tukuicin Naira miliyan 50 kan Ibn Muhammad, yayin da aka sanya Naira miliyan 10 kan Muhammad Jidda.

Sojojin sun bukaci jama’a su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai ta hanyoyin da aka tanada, tare da gargadin kada wani ya yi yunkurin kama wadanda ake zargin da kansa.

More from this stream

Recomended