

Ƴan takara biyu da suka tsaya takarar zaɓen gwamnan jihar Osun, Adewale Adebayo na jam’iyar APM da kuma Adedamola Adebayo na jam’iyar PDP sun janye daga zaɓen inda suka goyi bayan gwamnan jihar, Ademola Adeleke dake takara a karkashin jam’iyar Accord Party.
Adewale ya sanar da janye takarar tasa ne a wani taron manema labarai da ya kira ranar Alhamis inda ya ce ya ɗauki matakin ne bayan dogon nazari tare da tattaunawa da shugabannin jam’iya da kuma magoya bayansa.
Ya ce ya ɗauki matakin ba tare da fuskantar matsin lamba ba sai dan kawai fifita buƙatar jihar Osun fiye da ta ƙashin kansa .
Dan siyasar ya ce ya duba halin da ake ciki a siyasar jihar inda ya yanke hukuncin cewa gwamnan jihar na bukatar a sake bashi wata damar domin ya kammala muhimman ayyukan cigaba da ya fara.
A ƙarshe ya shawarci magoya bayansa da su zaɓi gwamna, Adeleke a zaɓen da za a gudanar na ranar Asabar.
Adedamola Adebayo ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen gwamnan jihar shima ya janye takarar tasa inda ya goyi bayan gwamna, Adeleke.
Adebayo ya bayyana haka ne a wurin wani taron manema labarai da ya kira a Osogbo babban birnin jihar
Ya shawarci mambobi da kuma magoya bayan jam’iyar PDP da su fito su kadawa Adeleke a zaɓen.