
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kwara ta kama wani da ake zargi da harkar garkuwa da mutane, Sanda Aliyu, yayin da yake ƙoƙarin sayen bindigar AK-47 a Ƙaramar Hukumar Kaiama ta jihar.
An kama shi ne a ranar 3 ga Agusta, 2026, bayan jami’an Sashen Yaƙi da Garkuwa da Mutane sun samu bayanan sirri kan shirin sayen makamin.
Kakakin rundunar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta ce Aliyu ya riga ya biya Naira miliyan 1.6 a matsayin wani ɓangare na kuɗin sayen bindigar kafin jami’an tsaro su kama shi.
Ta ce yayin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya bayyana cewa yana son mallakar AK-47 ɗin ne domin ya samu matsayi na shugabanci a cikin ƙungiyar masu garkuwa da mutane da yake ciki.
“Ya ce yana shirin daga baya ya bar ƙungiyar, ya kafa tasa ƙungiyar masu aikata laifuka kuma ya jagorance ta,” in ji ta.
Rundunar ta ce kama Aliyu ya hana kammala cinikin makamin, tare da taimaka wa bincike kan sauran mutanen da ke da hannu a shirin.
A halin yanzu, ana ci gaba da neman Aliyu Mohammed, wanda ake zargi da tattaunawa da Sanda Aliyu kan sayar da bindigar, bayan ya tsere.