
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta yi amfani da zaɓen gwamnan Jihar Osun wajen nuna irin shirin da ta yi domin babban zaɓen 2027.
Za a gudanar da zaɓen gwamnan Osun a yau, Asabar 15 ga Agusta, 2026, inda ’yan takara 15 za su fafata.
A cikin manyan ’yan takarar akwai Gwamna Ademola Adeleke na Accord Party, Munirudeen Bola Oyebamiji na APC da Najeem Salaam na ADC.
A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya buƙaci INEC ta tabbatar da cewa zaɓen ya kasance cikin ’yanci, adalci da gaskiya.
Shugaban ya kuma yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a da su fito cikin lumana, tare da buƙatar jami’an tsaro su kare masu kaɗa ƙuri’a da jami’an zaɓe.
Tinubu ya ce zaɓen Osun shi ne zaɓen da ya rage kafin babban zaɓen 2027, don haka ya kamata INEC ta yi amfani da shi wajen gwada shirinta.
Ya kuma umarci Sufeto-Janar na ’Yan Sanda da sauran hukumomin tsaro su samar da isasshen tsaro tare da hana masu tayar da hankali dagula zaɓen.
Ya ce sakamakon zaɓen dole ne ya kasance abin da ya dace da muradin al’ummar Jihar Osun.