Yan sanda sun kama wata mata da ake zargi da satar jariri a jihar Kebbi

Rundunar ƴan sandan jihar Kebbi ta kama wata mata mai suna, Khadijah Ibrahim mai shekaru 19 da ake zargi da hannu a sace wani jariri sabuwar haihuwa a garin Zuru dake jihar.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, SP Bashir Usman ya fitar ya ce matar ta fake da taimakawa Fatima Mohammed wacce ta haifi sabon jari inda ta ce za ta samo mata ruwan zafi ta yi wa jaririn wanka amma sai ta tsere da jaririn da aka haifa.

Usman ya kara da cewa wacce ake zargin ta dade tana fuskantar matsin lamba da kuma gori kan cewa bata taba haihuwa ba bayan da  duk sa’annin aurenta sun haihu.

” Haka ne ya sa  ta yaudari majinta har tsawon watanni 9 cewa tana da ciki bayan da Fatima Mohammed ta haihu sai ta ɗauke jariri ta kai masa a matsayin nata,” a cewar sanarwar

Ya ce an kama wacce ake zargin ne biyo bayan dogon bincike inda aka gano jaririn a wurinta kuma aka mayar da shi wurin mahaifiyarsa.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...