
Sanata Rufai Sani Hanga dake wakiltar mazabar Kano ta tsakiya a majalisar dattawa ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar adawa ta NDC.
Hanga wanda shi ne sanata ɗaya tilo na jam’iyar NDC daga arewacin Najeriya ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar a wata wasika mai ɗauke da kwanan watan 3 ga watan Agusta da ya aikewa da shugaban jam’iyar NDC na mazabar Dakata dake ƙaramar hukumar Nasarawa ta jihar Kano
Sanatan ya ce yin murabus din nasa daga jam’iyar ya fara aiki nan take.
A makon da ya wuce ne sanata Hanga ya yi wata ganawa da shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a fadar Aso Rock inda wasu ke hasashen cewa zai koma jam’iyar APC bayan ganawar.

