Yan sanda sun kama dillalan bindigogi a jihohin Filato da Taraba

Jami’an yan sanda sun samu nasarar kama masu safara da sayar da makamai a jihar Filato dama wasu sassan kasarnan.

An kama mutanen tare da bindiga kirar AK-47 guda hamsin da harsashi mai tarin yawan gaske.

Mutanen da aka kama sun hada da Hamza Zakari(Hazo) mai shekaru 20, Abubakar Muhammad ( da ake kira Fancy) da Umar Ibrahim mai shekaru 25 da kuma Muhammad Abdulkarim da aka fi sani da Dan Asabe mai shekaru 33 dukkanin su mazauna birnin Jos an kama su ne bayan da aka samu bayanan sirri akan ayyukan da suke aikatawa a Jos da kewaye.

Mutanen na daga cikin manyan masu samar da makamai ga bata gari a Jos dama sauran sassan kasar nan daban-daban.

Har ila yau rundunar yan sandan ta samu nasarar kama wasu mutane uku da suke sayar da bindigogi a jihar Taraba.

Mutanen sun hada da Bello Sani, Venet Puncab da kuma Yusuf Nahoda dukkansu na zaune ne a karamar hukumar Ibbi ta jihar Taraba.

More News

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...

Ortom ya shawarci Yahaya Bello da ya miƙa kansa ga EFCC

Tsohom gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, a ranar Lahadin da ta gabata, ya bukaci takwaransa na jihar Kogi, Yahaya Bello, da ya fito daga...