
Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kubutar da Aliyu Muhammad ma’aikaci a hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC wanda wasu yan bindiga su ka yi garkuwa da shi a karamar hukumar Gummi a a jihar Zamfara.
A cewar Zagazola Makama,dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro cewa an yi garkuwa da Muhammad ne a ranar 07 ga watan Yuni lokacin da yake yiwa hukumar NECO aiki.
Sanarwar ta ce Muhammad ya ɗauki lokaci mai tsawo yana aikin rarraba takardun jarrabawar a kowace shekara na hukumar shirya jarrabawar kammala sakandare ta ƙasa NECO kafin ayi garkuwa da shi.
Makama ya ruwaito cewa s ranar 7 ga watan Yuli da misalin karfe 03:30 na ranar gungun wasu yan fashin daji dake kan babura sama da 50 su ka kai farma kan wasu kauyuka dake gundumar Ruwan Bore a karamar hukumar Talata Mafara.
Yan bindigar sun kwashe shanu da dama a yayin da wata mata ta samu raunin harbin bindiga a lokacin farmakin.
Ya kara da cewa daga nan suka karasa karamar hukumar Gummi inda suka dauki Mohammed inda daga bisani aka gano matarsa ta aiki kirar Hilux cars a wajejen yankin Tafkin.
.

