Yan sanda sun ceto ma’aikacin hukumar INEC daga hannun ƴan bindiga a jihar Zamfara

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kubutar da Aliyu Muhammad ma’aikaci a hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC wanda wasu yan bindiga su ka yi garkuwa da shi a karamar hukumar Gummi a a jihar Zamfara.

A cewar Zagazola Makama,dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro cewa an yi garkuwa da Muhammad   ne a ranar 07 ga watan Yuni lokacin da yake yiwa hukumar NECO aiki.

Sanarwar ta ce Muhammad ya ɗauki lokaci mai tsawo yana aikin rarraba takardun jarrabawar a kowace shekara na hukumar shirya  jarrabawar kammala sakandare ta ƙasa NECO kafin ayi garkuwa da shi.


Makama ya ruwaito cewa s ranar 7 ga watan Yuli da misalin karfe 03:30 na ranar gungun wasu yan fashin daji dake kan babura sama da 50 su ka kai farma kan wasu kauyuka dake gundumar Ruwan Bore a karamar hukumar Talata Mafara.

Yan bindigar sun kwashe shanu da dama a yayin da wata mata ta samu raunin harbin bindiga a lokacin farmakin.

Ya kara da cewa daga nan suka karasa karamar hukumar Gummi inda suka dauki Mohammed inda daga bisani aka gano matarsa ta aiki kirar Hilux cars a wajejen yankin Tafkin.

.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]