Babbar Kotun Ɗaukaka Ƙara ta 1 da ke Gusau, Jihar Zamfara, ta yanke wa Abdulshakur Tukur da Abdullahi Buba hukuncin kisa ta hanyar rataya kan laifin kashe wani matashi, Ahmad Yakubu.
Kotun, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Kulu Isa Aliyu, ta same su da laifin kashe Ahmad a wani kangon gida da ke unguwar Barakallahu a Gusau ranar 13 ga Disamba, 2021.
Kotun ta ce an kuma cire wasu sassan jikin mamacin bayan kashe shi.
Baya ga hukuncin kisa, kotun ta yanke wa mutanen biyu hukuncin zaman gidan gyaran hali na shekaru bakwai bisa laifin haɗa baki wajen aikata laifi.
Lauyan gwamnati, Kabiru Samaila, ya ce ya gamsu da hukuncin, tare da bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjojin da kotun ta amince da su.
A nasa ɓangaren, lauyan waɗanda aka yanke wa hukuncin, Zakari Abubakar, ya ce zai nazarci hukuncin kafin yanke shawarar ɗaukaka ƙara.
Kotun ta kuma wanke Ahmad Tukur tare da sallamarsa saboda rashin isassun hujjojin da za su tabbatar da hannu a kisan. Aminu Baba, wanda aka zarge shi da sayen wasu sassan jikin mamacin, ya rasu ne a lokacin da yake tsare a gidan gyaran hali.
Kotu Ta Yanke Wa Mutum Biyu Hukuncin Rataya A Zamfara

