Yan sanda sun kuɓutar da mutane 5 da aka yi garkuwa da su a Lagos

Jami’an yan sanda daga rundunar yan sandan jihar Ogun da ta jihar Lagos sun samu nasarar ceto da wasu mutane biyar da aka yi garkuwa da su su ka kuma kashe masu garkuwar su huɗu a wani farmakin hadin gwiwa da su kai dazukan dake kan iyakokin jihohin biyu.

Farmakin da aka yiwa lakabi da Operation Kosaye an ƙaddamar da shi ne kasa da sa’o’i 48 ya mayar da hankali ne kan kawo ƙarshen ayyukan batagari a wajejen yankin Ogbere.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi rundunar yan sandan jihar Lagos ta ce an kai farmakin ne bisa dogaro da kwararan bayanan sirri inda aka samu nasarar kama wasu mutane hudu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma wasu su 84 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

Rundunar ta ce jami’an sun kuma samu nasarar gano bindigogi, harsashi da sauran kayayyaki a yayin farmakin.

Sanarwar ta kara da cewa rundunar za ta cigaba da zage damtse wajen ganin cewa batagari sun rasa mafaka.

More from this stream

Recomended