Jami’an tsaro sun kubutar da mutane 16 da aka yi garkuwa da su a Kogi

Jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji, yan sanda,sojan ruwa, da kuma yan bijilante sun samu nasarar kubutar da mutanen da basu gaza 16 baa da aka yi garkuwa da su a jihar Kogi.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Talata, Appolonia Anele mai riƙon muƙamin daraktan yaɗa labarai na rundunar sojan Najeriya ta ce anyi garkuwa da mutanen ne a ranar Talata lokacin da wasu hatsari suka tsare matafiya akan hanyar Ojuwo-Ajengo-Memarebo da Ojuwo-Itobe a ƙaramar hukumar Itobe ta jihar Kogi.

Anele ta ce  wani maharbi guda ɗaya ya rasa ransa a yayin da ɗan sanda guda ɗaya ya jikkata a yayin farmaki da jami’an tsaron su ka kai da ya kai ga kubutar da mutanen.

” A yayin wani aikin nema da kubutarwa dakarun sojan Najeriya dake aiki kafada da kafada da na rundunar sojan ruwa, rundunar yan sandan Najeriya, yan bijilante da kuma maharba sun samu nasarar kubutar da dukkanin fasanjoji 16 da masu garkuwa da mutane suka yi garkuwa da su a jihar Kogi,” a cewar sanarwar

Sanarwar ta kara da cewa mutanen da aka ceto sun hada da maza guda shida, mata shida da kuma ƙananan yara su huɗu.

Tuni aka mika su ga jami’an kiwon lafiya domin bincika lafiyarsu kafin a mika su ga yan uwansu.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...