
Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa ya yi watsi da rahoton dake ikirarin cewa ya yi niyar yin murabus daga kan kujerarsa.
Da yake magana da yan jaridar dake fadar shugaban ƙasa a ranar Talata a Abuja ministan ya bayyana rahoton a matsayin karya tsagoranta kuma ya ci alwashin ɗaukar matakin shari’a.
Musa wanda ya isa fadar shugaban ƙasar da misalin karfe 03:00 na rana kuma ya fice wajen karfe 04:00 na yamma ya ce ya yi mamaki kan yadda ake hasashen a kan wa’adinsa inda ya zargi masu yaɗa maganar da yin zagon ƙasa ga yaddar da jama’a ke yiwa gwamnati na ƙoƙarin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi ƙasar nan.
” Babu aikin da zan bari. Ban taba yin magana kan haka ba,ban san wane mutumin ne ba ya kawo wannan labarin, ” a cewar Musa lokacin da yake zantawa da yan jaridar dake fadar shugaban kasa.
” Koma su waye zamu dauki matakin shari’a akansu.Munyi mamaki kuma na kaɗu sosai dana samu labarin ban san daga ina ya fito ba.”
Musa ya bayyana ganawarsu da shugaban ƙasar ganawa ce da aka saba yi da ta mayar da hankalin kan yanayin tsaro kuma shugaban Tinubu ya gamsu da ƙoƙarin da dakarun soja su ke na shawo matsalar tsaro.
“But whoever it is, we will take legal action against them. We are surprised. I was shocked when I saw that. I don’t know where that came from.
“But you always expect that there will be people who will not be happy when things are going well. Security is improving, things are getting better, and for them, that is a sad point. They always want to make it look as if it is not so.”
Musa described his meeting with the president as a routine security briefing, saying Tinubu expressed satisfaction with the military’s performance and ongoing operations across the country.

