Sojoji sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi a Katsina

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi tare da kwato shanu 318 na sata bayan wani farmaki da suka kai sansanin yan ta’adda daban-daban a jihar Katsina.

A wata sanarwar da aka fitar ranar Juma’a rundunar sojan ta ce an kai farmakin ƙarƙashin rundunar samar da tsaro ta Operation Clean Sweep da ta haɗa rukunin dakarun kai farmaki da daukin gaggawa na birged ta 17 da  zaratan dakaru na musamman da kuma dakarun sojan sama na rundunar Operation Fansan Yamma.

Rundunar dakarun na cigaba da zafafa kai farmaki kan maboyar yan ta’adda ta hanyar yin amfani da bayanan sirri wajen wargaza batagari tare da dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin arewa maso yamma.

Sanarwar ta ce dakarun sojan sun samu nasarar kutsawa dajin Fafu inda su ka samu nasarar gano wata maɓoyar wani gawurtaccen dan bindiga da ake ajiye mutanen da aka yi garkuwa da su a cikin mawuyacin hali.

Dakarun sun gano wani mai suna Nura Yar’adua wanda aka ɗaure shi da sarka da kuma gawarwakin wasu mutane biyu.

Bayan bashi taimakon gaggawa an garzaya da shi asibitin Koyarwa na Katsina domin samun kulawar likitoci.

More from this stream

Recomended