Ginin bene mai hawa biyu ya ruguzo a Sokoto

Wani ginin bene da ake aikin ginawa ya ruguzo a ranar Laraba. Amma kuma babu a asarar rai ko jikkata faduwar benen dake kan titin Bauchi a cikin garin Sokoto.

Ginin ya ruguzo ne da misalin karfe 02:00 na rana jim kaɗan bayan ma’aikatan dake aiki a ciki sun fice biyo bayan gargadin da aka yi musu cewa ginin na shirin ruftawa bayan wasu alamomi da suka bayyana a ginin.

Lamarin da ya faru ya haifar da kai daukin gaggawa daga jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA, hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Sokoto SEMA, da hukumar da sauran hukumomin da abun ya shafa.

Bello Shehu wani kafinta dake aikin rufi a wurin ya bayyana cewa yana sama yana aikin rafta ya sauko domin ya yi Sallah.

Bayan ya sauko ne wasu dake kusa suka lura da halin da ginin yake ciki inda suka ankarar da ma’aikatan dake ciki.

Mintuna goma shabiyar da ficewarsu ne lamarin ya faru.

More from this stream

Recomended