‘Yan Sanda Sun Kama Sakataren Gwamnati Tare Da Wasu Kan Zargin Sayen Ƙuri’u





Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Osun ta kama Sakataren Gwamnatin Jihar, Teslim Igbalaye, tare da wasu mutane 5 bisa zargin hannu a harkar sayen ƙuri’u a Osogbo.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abiodun Ojelabi, ya ce an kama mutanen ne a wani samame da aka kai bayan samun sahihan bayanan sirri. Ya ce samamen ya nufi wani gida da ake alaƙanta da SSG, inda ake neman wani da ake nema ruwa a jallo bisa zargin hannu a manyan laifuka, ciki har da kisan kai.

A cewarsa, jami’an tsaro sun ƙwato N4,810,500, kwamfutar tafi-da-gidanka, na’urar kwafe da ta buga takardu, katunan PVC guda 2 da kuma kundin masu zaɓe na gundumomi 15.

Rundunar ta ce tana binciken yiwuwar aikata laifukan da suka shafi Dokar Zaɓe ta 2022, ciki har da zargin sayen ƙuri’u, haɗa baki wajen aikata laifi da kuma ɓoye wanda ake nema ruwa a jallo.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Osun, Ibrahim Gotan, ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa bincike zai gudana ba tare da nuna son kai ba, yana mai cewa duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi bisa tanadin doka.

More from this stream

Recomended