Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar.
A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban Najeriya kan ƙudirinsa na magance matsalolin tsaro, musamman hare-haren da ke shafar al’ummomin Kiristoci.
Trump ya kuma ce yana alfaharin mara wa Tinubu baya a yaƙi da ƴan ta’adda domin ƙarfafa Najeriya da bunƙasa ta.
Haka kuma, ya jaddada cewa dangantakar Amurka da Najeriya na da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci da matsalolin tsaro ke ƙaruwa a Yammacin Afirka da sauran sassan duniya.
Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

