An kama mutumin da  ya yi garkuwa da kansa don karɓar kuɗin fansa

Rundunar ƴan sandan jihar Ondo ta ce ta kama wani mutum mai shekaru 33 bayan da aka zarge shi da shirya yin garkuwa da kansa tare da karɓar kuɗin fansa daga yan uwansa

A wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Abayomi Jimoh mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Ondo ya ce wanda ake zargin mai suna Olawale Sikiru an kama shi tare da abokinsa da suka haɗa baki biyo bayan gudanar da cikakken bincike.

Jimoh ya ce a ranar 5 ga watan Yuli ne, Iyabo mahaifiyar wanda ake zargi ta shigar da korafi wurin ya sandan tana zargin cewa masu garkuwa da mutane sun yi garkuwa da ɗanta lokacin da yake tafiya aiki garin Igbara-Oke

Ya ce an tuntubi iyalan Sikiru inda aka buƙaci su biya kuɗin fansa naira miliyan ɗaya.

Mai magana yawun rundunar ya ce binciken da yan sanda masu bincike suka gudanar ta hanyar amfani da na’urori da kuma bayanan sirri  kan lambar wayar da aka nemi kuɗin fansar da ita ya kai ga kama Sikiru a ranar 7 ga watan Yuli inda aka tabbatar da shi ne ya shirya yin garkuwar.

Jimoh ya ce wanda ake zargin ya yi nasarar karɓar kuɗi har naira ₦50,000 daga yan uwansa a matsayin wani ɓangare na kuɗin fansa.

More from this stream

Recomended