Sowore ya yi alkawarin dawo da tallafin man fetur

Omoyele Sowore ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyar AAC ya ce zai dawo da tallafin man fetur matukar aka zabe shi shugaban ƙasa a zaben 2027.

Da yake magana lokacin da ya bayyana a gidan talabijin na Arise a ranar Talata Sowore ya yi zargin cewa har yanzu gwamnatin tarayya tana bayar da tallafin man fetur da kuma na takardar kuɗin Naira duk da ikirarin cire su da gwamnatin ke yi.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya kawo ƙarshen tallafin man fetur a ranar da aka rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasa.

Da aka tambaye shi ko zai dawo da tallafin man fetur Sowore ya ce “tabbas babu tantama,”

Ya yi ikirarin cewa gwamnatin kawai ta canzawa tallafin suna ne.

“Asali ma dai har yanzu suna biyan tallafi.kawai dai sun canza sunan da su ke kiransa ne,” ya ce.

“Ba wai kawai fetur suke bawa tallafi ba saboda babu wadatacce kuma basa iya ta ce shi a cikin ƙasa. Suna kuma tallafawa Naira. Wannan na daga cikin abu da baza su taɓa fada muku ba,”

Mai fafutukar kishin kasar ya ce tallafi ba abu ne marar kyau ba inda ya ce yakamata gwamnati ta tallafawa ƴan ƙasa masu ƙaramin ƙarfi.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...