Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ta kama wani matashi mai shekaru 21 mai suna Samson Onilewaji bayan an same shi da hannun mutum da aka yanke tare da wasu makamai da kayayyakin da ake zargin na sata ne.
Mai magana da yawun rundunar, Abimbola Adebisi, ta bayyana hakan a wata sanarwa da aka wallafa a shafin X na rundunar ranar Juma’a.
A cewar sanarwar, jami’an tsaro sun tare wata motar haya marar rajista mai ɗauke da fasinjoji shida a hanyar Lekki-Epe yayin gudanar da bincike na tsaro.
Rundunar ta ce wanda ake zargin ya amsa cewa ya yi wa mutum uku fashi tare da kwace musu kayayyakinsu, ciki har da na’urar POS da katunan ATM da aka gano a hannunsa.
’Yan sanda sun ce suna ci gaba da bincike domin gano mamallakin hannun da aka samu da kuma dalilin mallakarsa, tare da neman wasu da ake zargin suna da alaƙa da lamarin.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Tijani Fatai, ya buƙaci mazauna jihar su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai masu amfani domin taimakawa wajen hana aikata laifuka.
’Yan Sanda Sun Kama Wanda Aka Same Shi Da Hannun Mutum A Legas

